VOANews.com

Muryar Amurka ▪ Hausa Majiya Kwakkwara

11 Janairu 2009 

Yau A VOA:

Labarai Cikin Harsuna 45
Litinin Kotun Daukaka Kara Ta Afirka Ta Kudu Zata Yanke Hukumci Kan Shari'ar Jacob Zuma

11/01/2009

President of S. Africa's ruling party African National Congress, Jacob Zuma
Jacob Zuma
Litinin din nan wata kotun Afirka ta Kudu take shirin yanke hukumci dangane da wata karar da ta shafi zargin zarmiya da cin hancin da ake yi ma Jacob Zuma, mutumin da ake zaton zai tsaya takarar shugaban kasa.

Masu gabatar da kararraki sun roki Kotun Daukaka Kara ta Tarayya da ta kawar da hukumcin da wata karamar kotu ta yanke inda ta watsar da tuhumar da ake yi ma Zuma, shugaban jam'iyyar ANC mai mulkin kasar. A watan Satumba karamar kotun ta yanke wannan hukumci, abinda ya share ma Zuma fagen tsayawa takarar shugaban kasa.

Shugabannin ANC sun ce ko da an ci gaba aka tuhumi Zuma da wadannan laifuffuka, shi ne zai tsaya ma jam'iyyarsu takarar shugaban kasa.

Masu gabatar da kararraki suka ce Zuma ya karbi cin hanci a hannun wani kamfanin da ya samu aikin kwangila mai tsoka na sayo makamai. Zuma ya musanta aikata wani laifi, yana mai fadin cewa 'yan uba na siyasa ne kawai suke makarkashiyar ganin bayansa.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari

  Karin Labarai